Abin da Kwankwaso ya ce kan rashin tsaro karkashin mulkin Buhari

Поділитися
Вставка
  • Опубліковано 3 жов 2024
  • Tsohon gwamnan jihar Kano da ke arewacin Najeriya, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, ya nuna damuwa kan yadda sha'anin tsaro ke ci gaba da tabarbarewa a Najeriya musamman a arewacin kasar.
    Ya bayyana haka ne a wata tattaunawa ta musamman da BBC Hausa ranar Litinin.
    Sanata Kwankwaso yana gani barin matsalar da aka yi ta dauki lokaci ba tare da daukar mataki ba shi ya sa yanzu take neman gagarar hukumomi.
    Ya kara da cewa abubuwan da ke faruwa a Najeriya suna da ban mamaki, yana mai cewa daga lokacin da ya bar ma'aikatar tsaro a matsayin minista kawo yanzu bai taba zaton matsalar za ta tabarbare haka ba.

КОМЕНТАРІ • 49